in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya isa birnin Harare don ziyarar aiki
2015-12-01 17:33:15 cri
 

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Hararen kasar Zimbabwe da sanyin safiyar Talatar nan, domin fara ziyarar aiki.

A cikin jawabin da ya gabatar a filin saukar jiragen saman kasar, mista Xi ya ce Sin da Zimbabwe kawayen juna ne, kuma dankon zumunci da shugaba Robert Mugabe da tsoffin shugabannin Sin suka kulla, ya haifar da karuwar arzikin kasashen biyu.

Tun kafuwar dangantakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu tsawon shekaru 35 da suka shude, bangarorin biyu na baiwa juna taimako da boyon baya, tare da cin moriyar juna, da dogaro da juna, baya ga ci gaba mai armashi a fannoni daban-daban da suka samu, ciki hadda fannin siyasa, da tattalin arziki da ciniki, da musayar al'adu da dai sauransu. (Amina)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China