in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadar Afirka ta Kudu a Sin: Ana sanya ran cimma matukar nasara a ziyarar shugaban Sin a Afirka ta Kudu
2015-11-30 21:38:28 cri
Bisa goron gayyatar shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gudanar da ziyarar aiki a ranar 2 zuwa ranar 5 ga watan Disamba, tare da jagorantar taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afrika a birnin Johannesburg.

Yayin taron manema labaru da aka shirya game da hakan, jakadar kasar Afirka ta Kudu a Sin madam Dolana Msimang, ta bayyana cewa kasar ta na sanya ran cimma babban sakamako daga ziyarar ta shugaba Xi ta wannan karo.

Madam Dolana Msimang ta jinjinawa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu a cikin 'yan shekarun da suka wuce, tana mai cewa an samu babban ci gaba wajen raya dangantaka tsakanin Afirka ta Kudu da Sin tun daga shekarar 1998, lokacin da aka kulla huldar diplomasiyya tsakanin sassan biyu.

Kaza lika madam Msimang ta ce, wannan ne karo na biyu da shugaba Xi ya kai ziyara kasar Afirka ta Kudu, bayan ziyararsa a kasar a shekarar 2013. Ta ce kasar Afirka ta Kudu tana farin ciki tare da alfahari da hakan.

Madam Dolana, ta kara da cewa shugaba Xi zai jagoranci taron kolin Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a ranar 4 da 5 ga watan Disamba tare da shugaba Jacob Zuma. Ana sanya ran cewa, taron kolin zai samar da karin zarafi na samun ci gaban kasashen Afirka da na Sin baki daya. Da fatan taron kolin zai daga matsayin dangantakar dake tsakanin sassan biyu, domin samar da makoma mai kyau ga nahiyar Afirka. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China