in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba za a rage saurin yin mu'amala a tsakanin Sin da Amurka ba, in ji mataimakin ministan wajen Amurka
2015-10-03 13:37:56 cri
A ranar Jumma'an nan 2 ga wata, mataimakin ministan kula da harkokin yankin Asiya ta gabas da na tekun Pacific Daniel Russel ya bayyana cewa, an sami sakamako mai gamsarwa sosai a ganawar da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka yi a birnin Washington kwanan baya. Ya ce shugabannin biyu sun kuma tattauna kan sabanin dake tsakanin kasashen su kai tsaye kuma ba tare da rufe kome ba, abin da ya nuna cewa, ba za a rage saurin yin mu'amalar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka ba.

Tun daga ranar 22 zuwa ta 25 ga watan Satumba, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki a kasar Amurka, a yayin ziyararsa, bangarorin biyu sun cimma matsaya guda kan manyan harkoki da sakamakon ci gaba guda 49.

A ran Jumma'a 2 ga wata, Daniel Russel ya bayyana cewa, ba kawai shugabannin kasashen biyu sun amince da akwai sabanin dake tsakanin kasashesu ba, haka kuma za su dukufa wajen warware sabanin.

Bugu da kari, ya ce, za a ci gaba da bunkasa mu'amalar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka, kuma bisa shirin da aka tsara. A wani bangaren kuma nan gaba mataimakin ministan harkokin wajen kasar Amurka Anthony Blinken zai kai ziyarar aiki a kasar Sin da kuma kasashen Koriya ta Kudu da Japan. (Maryan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China