in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron tattaunawa karo na 8 game da harkokin Internet tsakanin kasashen Sin da Amurka a birnin Seattle
2015-09-24 11:23:33 cri
An shirya taron tattaunawa karo na 8 game da yanar gizo wato Internet a tsakanin kasashen Sin da Amurka a cibiyar kamfanin Microsoft da ke birnin Seattle a kasar Amurka. Kwararru a fannin Internet na kasashen Sin da Amurka sun halarci taron, inda direktan ofishin kula da yanar gizo na Sin Lu Wei ya yi jawabin mai taken "Amincewar juna da hadin gwiwa don samun moriyar juna", kana masana'antun Sin da Amurka guda 7 sun daddale yarjejeniyar hadin gwiwa a yayin taron.

A cikin jawabin, Lu Wei ya ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, kasar Sin na dagewa kan tabbatar da tsaron Internet, Sin da Amurka sun dora muhimmanci sosai game da wannan fanni, don haka ya kamata bangarorin biyu su tinkari matsaloli tare, gami da yaki da masu laifuffuka kan Internet.

A wata sabuwa kuma, Mr. Lu ya ruwaito shugaban Xi game da Sin ke tsayawa kan nuna adalci ga dukkan kamfanoni, ciki har da na kasashen waje da ke kasar, kana tana kokarin girmama da kare moriya da hakkinsu.

A nasa bangare, mataimakin ministan kasuwancin Amurka Bruce H. Andrews ya ce, Sin da Amurka manyan abokai ne a fannin tattalin arziki a karni na 21, idan suka gamu da matsaloli da kalubale, ya kamata a yi shawarwari da tattaunawa, ba ya fatan wadannan matsaloli za su kawo lahani game da hadin gwiwar cinikayya tsakanin kasashen biyu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China