in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar da shugaban Xi Jinping na kasar Sin zai kai kasar Burtaniya tana da ma'ana matuka
2015-10-01 18:00:19 cri
A kwanan baya ne, jakadan kasar Sin dake kasar Burtaniya Mr. Liu Xiaoming ya rubuta wani sharhi a mujallar "The World Today" ta hukumar nazarin harkokin kasa da kasa ta masarautar Burtaniya, inda ya nuna cewa, bisa gayyatar da sarauniya Elizabeth II ta Burtaniya ta yi masa ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyarar aiki kasar Burtaniya a watan Oktoban, kuma shi ne shugaban kasar Sin ya sake ziyarar kasar Burtaniya tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Jakada Liu Xiaoming ya ce, a lokacin da yake ziyara a kasar Burtaniya, shugaba Xi Jinping da firaministan kasar Burtaniya za su tsara matsakaita da manyan matakan bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu a nan gaba, kuma kasashen Sin da Burtaniya za su kara yin hadin gwiwa daga dukkan fannoni, ta yadda za a kara karfafa dangantakar abokantakar da aka kulla daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare.

Ana kuma fatan sakamakon wannan ziyarar aiki ta tarihi mai muhimmiyar ma'ana, dangantakar dake tsakanin kasashen Sin da Burtaniya za ta shiga wani lokaci mafi kyau har ya kasance mai fa'ida ga shiyya-shiyya da ma duniya baki daya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China