in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi bikin tunawa da 'yan mazan jiya a filin Tian'anmen
2015-09-30 11:06:41 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran manyan jami'an gwamnatin kasar sun halarci bikin tunawa da 'yan mazan jiya a ranar Laraban nan a filin Tian'anmen dake birnin Beijing, inda suka tuna tare da karrama wadanda suka sadaukar da rayuwa.

Wasu sojojin da suka ritaya da iyalan wasu mazan jiya da wakilai daga sassa daban daban sun hallara a filin domin bikin kasar karo na biyu na tunawa da 'yan mazan jiya a jajibarin ranar kafuwar kasar ta ranar 1 ga watan Oktoba.

Yan mazan jiyan kamar yadda gwamnati ta kira su, mutane ne da suka sadaukar da rayuwansu domin samar da 'yancin kasar da ci gabanta, har ma da walwalar al'umma na zamanin yanzu, ko kuma bayan yakin Opium na farko wato tsakanin shekara ta 1840-1842, an ce, Sin tana da wadannan mutane miliyan 20.

Majalissar wakilan kasar Sin ta amince da ranar 30 ga watan Satumbar bara ta zama ranar tunawa da 'yan mazan jiya.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China