Manzon musamman na shugaban Sin zai halarci bikin rantsar da shugaban Sudan
2015-05-28 19:52:32
cri
A yau Alhamis ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yayin taron manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing cewa, bisa gayyatar da shugaban kasar Sudan Omer Hassan Ahmed Elbashir ya yi wa kasar Sin, ministan kiyaye muhalli na kasar Sin Chen Jining zai halarci bikin rantsar da shugaban kasar Sudan da za a yi a ran 2 ga watan Yuni, a matsayin manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping. (Maryam)