in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta taya shugaban Sudan murnar lashe zaben shugaban kasar
2015-04-28 19:55:56 cri
A yau ne kasar Sin ta taya shugaba Omar al-Bashir na Sudan murnar lashe zaben shugaban kasar da aka yi, lamarin da ya ba shi damar sake wani sabon wa'adi na shugabancin kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Son Hong Lei wanda ya bayyana hakan a yau yayin taron manema labarai, ya kuma bayyana kudurin kasar Sin na bunkasa sabon ci gaba a hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Sudan.

Ya ce, kasancewar Sin muhimmiyar abokiyar Sudan, kasar ta Sin na mutunta zabin al'ummar Sudan kuma a shirye Sin take ta taimakawa kokarin Sudan na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, bunkasa tattalin arziki da inganta rayuwar al'ummar kasar.

A jiya ne hukumar zaben kasar Sudan ta ayyana Al-Bashir a matsayin mutumin da ya lashe zaben shugaban kasar bayan da ya samu kashi 94.5 cikin 100 na kuri'un da aka kada a zaben shugaban kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China