in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Al-Bashir ya kada kuri'a a zaben shugaban kasa da aka fara a Sudan
2015-04-13 19:57:59 cri
Shugaba Omar Al-Bashir na kasar Sudan ya kada kuri'arsa a birnin Khartoum a zaben shugaban kasa da 'yan majalissun dokokin kasar ta Sudan, wanda aka fara gudanarwa a Litinin din nan.

Jam'iyyun siyasar kasar 45 da suka hada da kananan jam'iyyu da dama ne dai suka shiga zaben na wannan karo.

Rahotanni sun bayyana 'yan takarar shugabancin kasar ta Sudan 16 ne za su fafata a zaben, ciki hadda da shugaba mai ci Omar Al-Bashir, ko da yake wasu daga jam'iyyun adawar kasar sun kautacewa shiga zaben.

Al'ummar kasar kimanin miliyan 13 da dubu dari 6 ne ake zaton za su kada kuri'unsu a zaben, a rumfunan zaben da yawansu ya kai 7000.

Bisa tsarin zaben dai za a fafata neman kujerun 'yan majalissar dokokin kasar 1,072, da kuma kujerun 'yan majalissar jihohi 2,235. Za kuma a ci gaba da kada kuri'u ya zuwa ranar Laraba, kafin kuma a fara kidayar kuri'u a ranar Alhamis. Kazalika ana fatan bayyana sakamakon zaben a ranar Litinin 27 ga watan nan.

Kungiyoyi da hukumomin kasa da kasa da dama ne dai ke sanya ido game da zaben, wadanda suka hada da wakilan IGAD, da na AU, da kuma na kungiyar kasashen Larabawa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China