in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar mai mulki a Sudan na shirin kafa sabuwar gwamnati
2015-05-02 19:54:09 cri
Jam'iyyar NCP mai mulki a kasar Sudan ta sanar da shirinta na kafa sabuwar gwamnati, bayan ta lashe babban zaben da aka gudanar cikin watan Afrilun da ya gabata, inda shugaban kasar mai ci Omar Hassan Ahmed Al-Bashir ya sake samun nasara a kuri'un da aka kada, zai kuma ci gaba da kasancewa shugaban kasar kuma jagoran jam'iyyar mai mulki.

Da wani ci gaban kuma, mataimakin shugaban jam'iyyar ta NCP Ibrahim Ahmed Ghandour, ya ce jam'iyyar tasu ta riga ta cimma matsaya daya da jam'iyyar adawa ta Umma, wadda ta amince ta goyawa shirin kafa sabuwar gwamnati baya.

Bugu da kari, Ghandour ya yi Allah wadai da tashe-tashen hankulan da dakarun SPLA suka haddasa a yayin babban zaben kasar, inda ya ce ba za a gudanar da shawarwari da kungiyar ba, har sai ta canja akidunta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China