in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta tura masu sa ido kan babban zabe a kasar Sudan
2015-04-14 11:15:54 cri
A jiya Litinin ranar 13 ga wata, kungiyar AU ta sanar da cewa, ta riga ta tura masu sa ido zuwa jihohi daban-daban na kasar Sudan, game da babban zaben da ake yi daga ranar 13 zuwa ranar 15 ga wata.

Bayan da aka samu goron gayyata daga gwamnatin Sudan, shugabar kwamitin kungiyar AU Nkosazana Dlamini Zuma ta amince da tura kungiya mai sa ido ta AU mai suna AUEOM zuwa kasar Sudan don babban zaben kasar da na majalissun kasar.

A ranar 10 ga wata, AU ta aika masu sa ido 20, wadanda suka fito daga kasashen Afrika 14 zuwa kasar Sudan don sa ido kan babban zaben kasar cikin wani gajeren lokaci, kuma wadannan mutane 20 sun wakilci kungiyar majalisar dokoki ta Pan-Afrika wato PAP, da hukumar kula da zaben ta EMBs da kungiyar kula da zamantakewar al'umma da jama'a ta CSOs.

Kungiyar AUEOM dake karkashin shugabancin tsohon shugaban kasar Nijeriya Olusegun Obasanjo ta isa birnin Khartoum a jiya, kuma za ta tuntubi masu zabe don sa ido game da ayyukan jefa kuri'a da kuma kidayar kuri'u.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China