in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana yin bikin matasa na ranar 4 ga watan Mayu a Beijing
2015-05-04 16:13:04 cri

Yau ne a jami'ar kimiyya da fasaha dake nan birnin Beijing aka gudanar da bikin ranar matasa ta ranar 4 ga watan Mayu mai taken "matasa suna ba da gudummawa wajen kawar da cutar kanjamau a duniya.

Kungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu na kasashen Sin da Afirka, Asusun taimakawa zaman takewa(ta UNAIDS) da kuma jami'ar kimiyya da fasaha ta Beijing ne suka kira bikin cikin hadin gwiwa, domin amsa kiran da MDD ta yi wa matasan kasa da kasa, da su kara sanin illar cutar kanjamau, da kuma taimakawa kasashen Afirka wajen yin rigakafi da kuma hana yaduwar cutar.

Mataimakin babban magatakardan MDD, kana babban darektan hukumar UNAIDS Michel Sidibe ya yi jawabi a yayin bikin cewa, ya kamata matasan kasa da kasa su hada kai domin kafa wani dandalin kawar da cutar kanjamau tsakanin matasa.

Bugu da kari, a yayin da ya ke jawabi, babban sakataren kungiyar 'yan kasuwa masu zaman kansu na Sin da Afirka Wang Xiaoyong ya ce, kasar Sin na taka muhimmiyar rawa wajen kawo karshen kamuwa da cutar kanjamau, kawar da nuna bambanci ga wadanda suka kamu da cutar, da kuma kawo karshen mutuwar mutane sakamakon kamuwa da cutar, dangane da haka, kungiyar za ta karfafa hadin gwiwa da hukumar UNAIDS kan taimaka wa kasashen Afirka guda takwas wadanda suka fi fama da cutar, da kuma kara zuba jari cikin shirin hukumar, ta yadda za a iya ciyar da aikin yin rigakafi da kuma hana yaduwar cutar kanjamau a Afirka gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China