Yayin harin na ranar Juma'a, wanda ya kasance na farko da mayakan kungiyar suka kai yankin kasar ta Nijar, sun yi yunkurin mamaye garuruwan Bosso da Diffa, garuruwan kan iyaka dake yankin kudu maso gabashin kasar.
Rahotanni sun ce dakarun hadin gwiwar Nijar da Chadi ne suka dakile farmakin 'yan Boko Haram din, kuma ya zuwa yanzu ba a bayyana rashin rayuka daga bangaren sojojin kasar Chadi ba. koda yake an ce musayar wutar ta ritsa da wani farar hula guda.