in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya dawo gida bayan ziyarar aiki a wasu kasashe
2014-12-21 16:51:42 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya dawo nan birnin Beijing a jiyar Asabar bayan kammala ziyarar aikin da ya gudanar a wasu kasashe.

Rahotanni sun bayyana cewa, firaministan ya gudanar da ziyara a kasashen Kazakhstan da Serbia, inda aka cimma nasarori masu yawa, yayin ganawar firaministan na Sin da takwaransa na kasar Kazakhstan a karo na biyu. Baya ga hakan, Li Keqiang ya kuma halarci taron shuagabannin mambobin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai karo na 13, da aka gudanar a kasar ta Kazakhstan, da kuma taron shugabannin kasar Sin da na kasashen gabashi da tsakiyar Turai, da ya gudana a kasar Serbia.

Kaza lika firaministan na Sin ya halarci taron shugabannin shirin samar da ci gaban hadin gwiwar tattalin arzikin kasashen dake kewayen kogin Mekong, karo na biyar da aka gudanar a kasar Thailand. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China