in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya gabatar da ra'ayoyi biyar kan warware matsalar Afghanistan
2014-10-31 16:06:35 cri
An gudanar da taron ministocin harkokin waje karo na 4 kan shirin Istanbul game da batun Afghanistan a safiyar yau Jumma'a 31 ga wata a nan birnin Beijing, inda firaministan kasar Sin Li Keqiang, da shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani suka halarci taron.

Li Keqiang ya gabatar da ra'ayoyin kasar Sin biyar kan warware matsalar Afghanistan, wato a bari jama'ar Afghanistan su gudanar da harkokin kasa da kansu, da sa kaimi ga kokarin samun sulhu, da gaggauta sake raya tattalin arzikin kasa, da neman hanyar samun bunkasuwa da kuma kara yin amfani da taimakon da kasashen waje suke baiwa kasar

An tsara shirin Istanbul a shekarar 2011, wanda shi ne shirin hadin gwiwa daya kawai da kasashen da batun Afghanistan ya shafa suke jagoranta a halin yanzu. Wannan ne karo na farko da kasar Sin ta karbi bakuncin wannan taro, kana shi ne taro na farko da aka gudanar kan batun Afghanistan bayan da aka kafa sabuwar gwamnatin kasar, inda ministocin harkokin waje da wakilai na kasashe 14 dake cikin tsarin shirin Istanbul, da sauran kasashe 16, kungiyoyin kasa da kasa da wasu yankuna 12 suka halarci wannan taron. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China