Za a yi amfani da kudaden ne a kasashen uku da suka hada da Saliyo, Liberia da kuma Guinea don taimaka musu ta yadda za su tunkari cutar Ebola.
Matakin da gwamnatin kasar Sin ta dauka yana daya daga cikin shirin taimako zagaye na uku da gwamnatin kasar Sin ta samar wajen yaki da cutar Ebola, da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar a ran 18 ga watan Satumba, kuma yana daga cikin amsa kiran da hukumar WHO ta yi wa kasashen duniya wajen ba da taimako ga kasashen Afirka da abin ya shafa. (Maryam)