in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa Sudan ta Kudu
2014-09-25 20:30:31 cri
A yau Alhamis 25 ga watan ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana yayin taron manema labarai a birnin Beijing cewa, bisa bukatar MDD ta yi wa kasar Sin za ta kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya guda 700 zuwa kasar Sudan ta Kudu don kiyaye zaman lafiya da zaman karko a kasar, musamman ma kiyaye rayukan fararen hulan kasar da kuma taimaka wa harkokin jin kai. A halin yanzu, kasar Sin na kokarin yin shawarwari da MDD kan yadda za a gudanar da aikin.

Ya zuwa yanzu, MDD ta gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya a nahiyar Afirka guda 9, inda kasar Sin ta halarci 7 daga cikinsu, dangane da lamarin, Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin ta kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa kasar Sudan ta Kudu, wannan wani muhimmin mataki ne da Sin ta dauka wajen goyi bayan MDD kan aikinta na kiyaye zaman lafiya. Haka kuma, kasar Sin za ta ci gaba da halartar aikin kiyaye zaman lafiya da MDD take gudanarwa don ba da gudummawa kan kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa, musamman ma a nahiyar Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China