in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD na maida hankali wajen daidaita zaman lafiya a shiyyar Abyei
2014-05-30 16:19:11 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya zartas da wani kuduri a ranar 29 ga wata, inda aka tsawaita wa'adin sojojin wucin gadi na kiyaye tsaro na MDD dake shiyyar Abyei zuwa ranar 15 ga watan Oktoba na bana, kana kuma yana la'akari da sake daidaita wannan tawagar sojojin wanzar da zaman lafiya dake yankin.

Kudurin ya bukaci kasashen Sudan da Sudan ta Kudu da su kafa hukumar gudanar da harkokin shiyyar Abyei da majalisar dokokin shiyyar cikin sauri. Kuma ya kamata a kafa ofishin 'yan sanda a shiyyar don tabbatar da tsaron lafiyar shiryyar ciki har da na muhimman ayyukan hakar man fetur. Kana kwamitin sulhu ya jaddada cewa, baya ga sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD dake shiyyar da ofishin 'yan sanda na wurin, bai kamata a jibge sojoji da dakaru a wannan shiyya ba.

Hakazalika kuma, kwamitin sulhu ya bayyana cewa, zai yi bincike kan ka'idojin sojojin kiyaye zaman lafiya dake shiyyar Abyei, da sake daidaita sojojin bisa yadda kasashen Sudan da Sudan ta Kudu suka yi alkawarin janye sojoji daga yankin iyakar kasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China