in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi kira ga bangarori daban daban na Sudan ta Kudu da su bi yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2014-08-09 17:03:18 cri
Kwamitin sulhun MDD ya ba da sanarwar a ranar 8 ga wata cewa, ana mai da hankali sosai kan bala'in jin kai da ake fuskanta a sakamakon rikicin Sudan ta Kudu, kuma ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su bi yarjejeniyar tsagaita bude wuta da suka cimma.

Sanarwar ta ce, kwamitin sulhu yana damuwa da mai da hankali sosai kan tabarbarewar yanayin tsaro da na siyasa da abkuwar bala'in jin kai a sakamakon rikicin da ya barke a Sudan ta Kudu, kuma ya yi Allah wadai da ayyukan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta sau da dama, tare da jaddada cewa, ba za a amince da yunkurin shugaban Sudan ta kudu Salva Kiir Mayardit da tsohon mataimakinsa Khaled Mashaal na daidaita rikicin kasar ta hanyar makamai.

Dadin dadawa, sanarwar ta ce, kwamitin sulhu ya yi kira ga shugaba Kiir da mataimakinsa Mashaal da sauran bangarorin kasar da su bi yarjejeniyar tsagaita bude wuta, su yi hakuri su tare da aiwatar gudanar da shawarwarin da aka cimmasulhu a birnin Addis Ababa cikin lumana, domin cika alkawarinsu na kafa hadaddiyar gwamnatin rikon kwarya kafin ranar 10 ga wata. Kuma kwamitin sulhu ya y i kashedin daukar matakai kan wadanda suke kawo illa ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da tsaron kasar Sudan ta Kudu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China