in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron kwamitin harkokin sojan NATO a kasar Lithuania
2014-09-21 17:02:24 cri
Jiya Asabar 21 ga wata, an yi taron manyan hafsoshin kwamitin harkokin sojan kungiyar yarjejeniyar Atlantic ta Arewa ta NATO a babban birnin kasar Lithuania, Vilnius, inda aka tattauna kan harkokin tsaron yankin da na ciyar da shirin kafuwar wata rundunar sojojin ta matakin share fage, domin fuskantar matsalolin tsaro yadda ya kamata da dai sauransu.

A yayin taron maneman labaran da aka yi bayan taron, shugaban kwamitin harkokin sojan kungiyar NATO Knud Bartels ya bayyana cewa, abubuwan da aka tattauna a yayin taron sun hada da batutuwan kasashen Rasha, Ukraine da na yankunan Sahel, Gabas ta Tsakiya, Afirka ta arewa da kuma Asian-Pacific.

Ya kuma kara da cewa, babban batun da aka tattauna a yayin taron shi ne, yadda za a iya ciyar da shirin kafuwar wata rundunar sojojin ta matakin share fage, ya ce, kungiyar NATO ta iya tura sojoji da kayayyakin soja a wuraren dake bukata cikin gajeran lokaci.

Yayin da yake tsokaci kan batun Afghanistan, Mr. Bartels ya bayyana cewa, kungiyar NATO za ta samar da horaswa ga sojojin kasar Afghanistan bayan ta janye sojojinta daga yankin.

Ko wace shekara, kwamitin harkokin sojan kungiyar NATO na gudanar da tarukan manyan hafsoshin kungiyar sau uku, biyu daga cikinsu ana yin su a birnin Brussels, dayan kuma ana yinsa a tsakiyar watan Satumba a wata mambar kasa ta kungiyar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China