in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Pakistan ta sanar da sake yarda da kungiyar NATO ta yi sufurin kayayyakinta ta ratsa kasar
2012-07-04 15:26:00 cri
Ranar 3 ga wata, ministan watsa labaru na kasar Pakistan Qamar Zaman Kaira ya sanar da cewa, kasar ta yarda da sake bude hanyar zuwa Afghanistan wadda kungiyar NATO za ta bi wajen sufurin kayayyaki, saboda sakatariyar harkokin waje ta kasar Amurka Hillary Clinton ta yi ahuwa kan harin da NATO ta kaiwa wata tashar bincike dake kasar a watan Nuwanba na shekarar bara.

Qamar Zaman Kaira ya ce, kwamitin tsaron kasar Pakistan ya yi maraba da abin da Hillary Clinton ta yi, kuma taron ya yanke shawarar sake bude wannan hanya. Ya ce, wannan abu zai yi amfani wajen sa kaimi ga shimfidar zaman lafiya a Afghanistan, amma, kwamitin ya yanke shawara cewa, ba za ta yarda ba idan NATO ta yi sufurin makaman kare-dangi ta hanyar ratsa Pakistan.

Hillary Clinton ta tabbatar da wannan labari a ran 3 ga wata. Kuma ta gamsu da rawar da Pakistan ta taka wajen yaki da ta'addanci, kuma ta jaddada cewa, Amurka za ta yi hadin kai da Pakistan don yaki da ta'addanci da goyon bayan Afghanistan wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tare kuma da kara yin mu'ammala tsakaninsu a fannin cinikayya da zuba jari.

A wannan rana kuma, shugaban NATO Anders Rasmusen ya nuna maraba da shawarar da Pakistan ta yanke.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China