in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata koto a Masar ta yanke wa shugaban kungiyar 'yan uwa Musulmi hukuncin daurin rai da rai
2014-08-31 16:59:49 cri
Wata koton hukunta manyan laifuffuka a lardin Giza dake kasar Masar, ta yankewa tsohon shugaban babbar hukumar ba da shawara ta kungiyar 'yan uwan Musulmi Mohamed Badie da wasu mambobin kungiyar daurin rai da rai.

Kotun ta yankewa Badie da wasu sauran shugabannin kungiyar su 8 hukuncin daurin rai da rai ne, bayan da wata kotun ta yanke musu hukuncin kisa a watan Yunin da ya gabata. Baya ga wadannan jagorori na kungiyar ta 'yan uwa musulmi, kotun ta kuma yankewa wasu magoya bayan kungiyar su 6 hukuncin kisa.

Shi dai hukuncin baya, da waccan kotu ta yankewa wadannan shugabanni da magoyon bayan kungiyar 'yan uwa Musulmi a watan na Yuni, ya biyo bayan samun su da ta yi, da lafin jagorantar hare-hare, a wani wurin kusa da Masalacin lardin Giza a watan Yulin bara, kafin daga bisani a sauya hukuncin bisa shawarar shugaban addinin kasar.

Kotu mai hukunta manyan laifuffuka dake El Minya dai ta yankewa Mohamed Badie hukuncin kisa ne a watan Yunin da ya shude, bayan da ta tabbatar da zargin da aka yi masa na shirya kaddamar da hare-hare, da kisan 'yan sanda da dai sauransu.

Tun dai lokacin da rundunar sojan kasar Masar ta hambarar da Mohamed Morsi daga mukaminsa na shugabancin Masar a watan Yulin shekarar da ta gabata kawo yanzu, magoyon bayansa ke ci gaba da gudanar da zanga-zanga a sassan kasa akai akai. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China