in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da sabuwar majalisar zartaswar kasar Masar
2014-06-17 20:49:47 cri
A yau Talata ne aka rantsar da sabuwar majalisar zartaswar kasar Masar karkashin jagorancin firaminista Ibrahim Mahlab. Yayin da ministocin kudi da na tsaron kasar suka ci gaba da rike mukamansu karkashin sabon shugaban kasar Abdel-Fattah Al-Sisi.

Mahlab wanda ya yi aiki na tsawon watanni biyar a matsayin firaministan rikon kwaryar kasar zai ci gaba da rike wannan mukami, bayan da Al-Sisi ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar.

Sabuwar majalisar dai tana kunshe ne da ministoci 34, 13 daga cikinsu sabbi ne sai kuma mata 4 kacal.

An kuma nada Ashraf Salman a matsayin sabon ministan kula da harkokin zuba jari, da tsohon jakadan kasar Masar a kasar Amurka Sameh Shukri wanda aka nada a matsayin sabon ministan harkokin waje. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China