in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasashen Afirka su warware matsalolin Afirka da kansu
2014-06-27 15:41:17 cri
Shugaban kasar Masar Abdel- Fattah al-Sisi ya bayyana a gun taron koli na kungiyar AU a ranar 26 ga wata cewa, kamata ya yi kasashen Afirka su warware rikice-rikice da ta'addanci da suke fuskanta bisa tsarin kansu.

Al-Sisi ya ce, kasar Masar tana kokarin yin hadin gwiwa tare da sauran kasashen Afirka don inganta karfin Afirka a fannonin magance rikicin diplomasiya, tashe-tashen hankali da ta'addanci ta yadda ake iyar sake gina da bunkasa kasashen bayan rikici.

Hakazalika kuma shugaban Masar ya kara da cewa, game da barazanar da ta'addanci ke kawo wa kasa da kasa, tilas ne kasashen Afirka su tsaya tsayin daka kan yin tir da duk wani nau'in ta'addanci, da kara yin hadin gwiwa, da sa kaimi ga kasa da kasa wajen kara yaki da ta'addanci domin tabbatar da tsaron fararen hula da bunkasa tattalin arzikinsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China