in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake dawo da Masar cikin kungiyar AU
2014-06-18 20:52:09 cri
Mahukuntan kasar Masar sun yi maraba da shawarar da kungiyar AU ta yanke na sake dawo da kasar cikin harkokin kungiyar bayan dakatar da ita da aka yi na tsawon shekara guda.

Ma'aikatar harkokin wajen kasar Masar ta bayyana cikin wata sanarwa cewa, an yanke wannan shawara ce ganin yadda kasar ta gudanar da kuri'ar raba gardama kan kundin tsarin mulkin kasar da zabe da kuma rantsar da sabon shugaban kasar da aka gudanar.

A ranar Talata ne kwamitin zaman lafiya da tsaro na kungiyar ya yanke shawarar sake dawo da kasar cikin harkokin kungiyar, bayan da aka dakatar da ita a watan Yulin da ya gabata, sakamakon hambarar da zababben shugaban kasar Mohamed Morsi da sojojin kasar suka yi biyo bayan wani boren gama gari da aka yi game da mulkinsa na shekara guda kacal. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China