Madam Byrs ta bayyana cewa, samarwa 'yan kasar kimanin miliyan 4 da dubu 250 da 'yan gudun hijira na kasar miliyan 2 da dubu 900 wadanda suka gudu zuwa sauran kasashe, kalubale ne kuma wani aiki dake cikin gaggawa ga hukumar WFP. Tana mai cewa, hukumar na bukatar kudi dala miliyan 35 a ko wane mako domin biyan bukatun wadannan mutane, don haka ana bukatar samun tallafin da ya kai dala biliyan 2 a wannan shekara domin samar da abinci ta yadda za a samu damar sasanta halin da ake ciki a kasar.
Ban da haka, hukumar na nuna damuwa sosai kan lafiyar jikin 'yan kasar Sham da rikicin ke dabaibaye, ganin yadda ta yi iyakacin kokarin samar da tallafi ga mutanen dake kewaye da birnin Damascus a watannin da suka gabata, amma ba ta cimma nasara ba. (Amina)