in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na kokarin sauke nauyin dake wuyanta, in ji babban jami'in kasar Sin
2013-11-05 16:46:22 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana a jiya Litinin 4 ga wata cewa, a matsayinta na kasar dake rike da shugabancin karba-karbar a kwamitin sulhu na MDD, Sin na kokarin tabbatar da ayyukan kwamitin tare kuma da sauke nauyin dake wuyanta na kiyaye zaman lafiyar duniya da tsaro bisa ka'idar adalci, bude kofa da sauransu.

A wannan rana Mista Liu ya jagoranci taron kwamitin, inda aka zartas da shirin ayyukan da za a yi a watan Nuwamba. Daga baya, a gun taron manema labaru da aka yi bayan taron, Liu Jieyi ya bayyana cewa, kwamitin zai sha aiki a watan Nuwamba, inda za a kira taruruka har 30 wadanda za su shafi manyan batutuwa fiye da 20, daga cikinsu, akwai manyan batutuwa dangane da Afrika da batun yankin Gabas ta Tsakiya za su zama muhimman batutuwa a watan Nuwamba.

Game da kokarin da kotun hukunta manyan laifufuka ta kasa da kasa take yi na gurfanar da shugaban kasar Kenya a gaban kotun, a nasa bangare, Liu Jieyi ya nuna cewa, kasashen Afrika mambobin kwamitin sun riga sun gabatarwa kwamitin daftarin shiri, wanda suka nemi kotun da ta jinkirta lokacin gurfanar da shugaban Kenya a gaban kotun, kwamitin zai tattauna da bangarori masu ruwa da tsaki kan lamarin. Mista Liu ya kara da cewa, 'yan kasar Kenya ne suka zabi shugabansu, ya kamata a mutunta zabinsu. Sin sahihiyar abokiyar kasashen Afrika ce, ta fahimci damuwar Kenya da kungiyar tarayyar Afrika wato AU, kuma tana goyon baya kwamitin da ya amsa bukatun Kenya da AU yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China