in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ta cimma nasarar yaki da cutar Malaria
2013-10-10 15:30:41 cri
A ranar 9 ga wata, bisa wani rahoton da taron yaki da cutar Malaria ta kasashen Afrika da aka yi a birnin Durban mai tashar jiragen ruwa na Afrika ta Kudu, an ce, kasar Afrika ta Kudu ta samu nasara wajen yaki da cutar Malaria, kuma a cikin shekaru 12 da suka gabata, yawan mutanen da suka rasu sakamakon cutar ya ragu da kashi 85 cikin 100.

Rahoton ya bayyana cewa, mutane 70 ne kawai suka mutu a kasar a shekarar bara sakamakon cutar Malaria, yayin da a shekarar 2000, wannan adadi ya kai 460. A yankunan da aka fi samun cutar, yanzu, yawan mutanen da suka kamu da cutar ya ragu zuwa kasa da kashi 0.1 cikin 100.

Ministan kiwon lafiya na kasar Afrika ta Kudu Aaron Motsoaledi ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta yi shirin kawar da cutar Malaria zuwa shekarar 2018. Matakan da kasar ta dauka wajen cimma wannan buri sun hada da kashe sauro dake yada cutar, kyautatuwar yanayin kiwon lafiya na jama'a, kara fadakar da jama'a, da yin kokarin samar da jinya ga wadanda suka kamu da cutar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China