in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin Goldman Sachs ya yi nazari kan tattalin arzikin Afrika ta Kudu cikin shekaru 20 da suka gabata
2013-11-05 15:22:35 cri
A ranar 4 ga wata, shahararren bankin saka jari na duniya Goldman Sachs ya fid da wani rahoto game da nazarin tattalin arzikin kasar Afrika ta Kudu cikin shekaru 20 da suka gabata, inda ya bayyana kalubalen da tattalin arzikin kasar ke fuskanta, ciki har da yawan mutanen da suka rasa guraben aikin yi mai yawa, da wadanda albashinsu bai taka kara ya karya ba.

Wannan rahoto ya bayyana cewa, sakamakon kammala tsarin nuna bambancin launin fata a kasar Afrika ta Kudu cikin shekaru 20 da suka gabata ya sa, tattalin arzikin kasar ya samu ci gaba cikin hanzari, kuma yawan tattalin arziki da aka samu ya ninka sau 2. Amma wannan rahoto ya ci gaba da nuna cewa, tattalin arzikin kasar na ci gaba da fuskantar kalubaloli da dama. Yanzu, yawan mutanen da suka rasa guraben aikin yi ya zarce kashi 24 cikin 100, cikinsu, akasarinsu matasa ne. A sa'i daya kuma, akwai babban gibin a tsakanin masu kudi da talakawa, kuma kashi 85 cikin 100 na bakaken fata na kasar, albashinsu kalilan ne, yayin da kasha 87 cikin 100 na fararen fata, albashinsu ya ked a yawa.

Haka kuma, wannan ra'ayi ya dace da ra'ayin gwamnatin kasar Afrika ta Kudu. A watan Oktoba na bana, shugaban kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma ya bayyana cewa, yanzu,matsakaicin albashi na ko wane gida na fararen fata ya ninka sau 6 da takwarorinsu na bakaken fata, kuma al'ummar kasar na fuskantar talauci da rashin samun daidaito, da rashin samun guraben aikin yi, sannan da rashin samun fahimta.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China