in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron ministocin harkokin wajen kasashe 11 na kungiyar abokan kasar Sham a birnin London
2013-10-23 16:43:30 cri
Ministocin harkokin waje ko wakilan kasashe 11 dake cikin Kungiyar abokan kasar Sham ciki hadda Birtaniya, da Amurka da sauran wasu kasashen yamma da Saudiya, da Masar da sauran kasashen Larabawa, sun yi taro a birnin London a ran 22 ga wata.

Taron wanda ya maida hankali ga tattauna hanyoyin warware rikicin kasar ta Sham, da batutuwan da suka shafi taro na biyu da za a yi a birnin Geneva. Amma har ila yau kungiyar 'yan adawa ta kasar Sham ba ta yi alkawarin shiga taron ba tukuna.

Haddadiyar sanawar da aka bayar bayan taron ta yi kira da a kara baiwa 'yan adawa goyon bayan a fannin aikin soja, da siyasa, da kuma taimakawa musu wajen biyan bukatun jama'ar da ke shiyyoyin da suke mallaka, tare kuma da kafa gwamnatin wucin gadi cikin 'yan watanni masu zuwa, amma ba a gabatar da wa'adi na karshe ba cikin sanarwar.

Da tsokaci kan taron, shugaban zaman, kuma ministan harkokin wajen kasar Birtaniya William Hague, ya bayyana cewa, mahalarta taro sun kai ga cimma matsaya guda, musamman wajen karfafa hadin kai da sa kaimi ga aikin shimfida zaman lafiya a kasar Sham karkashin jagorancin MDD. Sa'an nan bangarori daban-daban sun yi kira ga sassan biyu da ke adawa da juna a kasar ta Sham da su shiga taro karo na biyu na kasa da kasa da za a yi a birnin Geneva a wata mai zuwa. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China