in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ta sanar da yanke huldar diplomasiyya da shugaba al-Assad na kasar Sham
2013-06-16 16:54:44 cri
Shugaban kasar Masar Mohamed Morsi ya sanar a daren ranar 15 ga wata a birnin Alkahira cewa, gwamnatinsa ta tsaida kudurin yanke dukkan huldar diplomasiyya tsakaninta da gwamnatin Bashar al-Assad na kasar Sham, ta kuma kirawo jakadanta dake Syria, tare da kuma rufe ofishin jakadancin kasar dake Syria.

Morsi ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Masar, jama'a da kuma sojojin kasar sun nuna goyon baya ga jama'ar kasar Syria a zabin da suka yi, kana ya jaddada cewa, kasarsa ba ta da yunkurin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasarta Sham.

Morsi ya nanata cewa, kasarsa ba ta goyon bayan dukkan wani aikin soja da na siyasa da sauran kasashen duniya da kungiyoyi suka yi a kasar Syria, kana ya yi kashedi ga kungiyar Hezbollah da ta dakatar da tsoma baki kan harkokin kasar Syria, ya kuma bukaci dakarun kungiyar da su janye daga kasarta Sham ba tare da bata lokaci ba.

Ban da wannan kuma, Morsi ya yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakai don magance tsanantar halin da kasar Syria ke ciki, ya kalubalanci kwamitin sulhu na MDD da ya zartas da kudurin kafa yankin hana zirga-zirgar jiragen sama a kasar Sham. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China