in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Nijeriya ya taya Robert Mugabe murnar ci gaba da mulki a matsayin shugaban kasar Zimbabwe
2013-08-06 14:19:09 cri

Hukumar zabe ta kasar Zimbabwe ta sanar a ran 3 ga wata cewa, shugaba mai ci Rober Mugabe ya lashe zabe da aka yi a ran 31 ga watan Yuli. Shugaban kasar Nijeriya Goodluck Jonathan ya yi maraba da sakamakon zabe, kana ya taya Robert Mugabe murnar ci gaba da mulki.

A cikin wata sanarwar da mai ba da shawara na musamman ga shugaban kasar Nijeriya kan harkokin yada labarai da fadakarwa ya bayar, Goodluck Jonathan ya kalubalanci shugaba Robert Mugabe da jam'iyyarsa ta ZANU-PF da su dukufa kan tabbatar da zaman alheri tsakanin jama'a da samun bunkasuwar kasar.

A cikin sanarwar, Goodluck Jonathan ya yi kira ga Robert Mugabe da ya tabbatar da cewa duk wani mutum ko jam'iyya wanda bai yarda da sakamakon zaben ba, da su bayyana burinsu ta hanyar da ta dace. A sa'i daya kuma, yana fatan shugaban babbar jam'iyya mai adawa, Morgan Tsvangirai da ya dauki mataki da ya dace domin bayyana korafinsa, saboda duk wani mataki da ba bisa doka ba, zai iya haifar da rikicin siyasa a kasar. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China