in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira da a kammala babban zaben kasar Zimbabwe cikin lumana
2013-08-03 17:02:39 cri
A ranar 2 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da wata sanarwa ta kakakinsa, inda ya yi kira ga kasar Zimbabwe da ta warware matsalolin da aka samu a babban zaben kasar cikin adalci, da kuma kammala zaben cikin lumana.

Sanarwar ta ce, Ban Ki-moon ya sa lura sosai kan babban zaben kasar Zimbabwe, da nuna yabo ga jama'ar kasar da su jefa kuri'u cikin lumana. Kana yana fatan jama'ar kasar Zimbabwe za su ci gaba da kwantar da hankalinsu yayin da ake kidaya kuri'u har zuwa lokacin kammala zaben. Kuma Ban Ki-moon ya yi kira ga shugaba, firaministan kasar na yanzu da jam'iyyu daban daban na kasar da su tabbatar da cika alkawarinsu na gudanar da zaben cikin lumana, da kira ga masu goyon bayansu da su kiyaye kwanciyar hankali.

Sanarwar ta kara da cewa, MDD tana son shugabannin kasar Zimbabwe za su kiyaye nauyi dake kansu da gudanar da ayyukan siyasa, kana su zama masu la'akari da ra'ayoyin bangarori daban daban, ci gaba da aiwatar da manufofin gudanar da ayyuka ta hanyar demokuradiyya da yin kwaskwarima, da kuma sa kaimi ga farfado da tattalin arzikin kasar don amfanin dukkan jama'ar kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China