in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mugabe na Zimbabwe ya sanar a gangamin karshe cewa bakaken kasa keda mallakar ma'adinai
2013-07-29 10:53:40 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe a ranar lahadin nan 28 ga wata wajen gangamin karshe na yakin neman zaben da za'a gudanar a ranar laraban nan mai zuwa 31 ga wata inda yake sa ran sake samun nasarar cigaba da mulkin sa da yanzu haka yayi shekaru 33 yana yi, ya jaddada cewa bakaken al'ummar kasar ne keda mallakar ma'adinai.

Mugabe dan shekaru 89 a duniya,ya sheda ma duban magoya bayansa da suka taru a filin wasa dake Harare babban birnin kasar cewa zai tabbatar da cewa bakaken fata 'yan asalin kasar ne kawai zasu mallaki dukiyar kasar koda kuwa zasu hada gwiwa da kamfanonin kasashen waje ne domin samun isassun jari.

A cewar Mista Mugabe, albarkatun kasa na jama'r kasashen ne kuma ya fi muhimmanci idan an kwatanta da jarin da kasashen waje zasu zuba. Kasar Zimbabwe wadda keda albarkatun kasa na lu'u lu'u da zinari tana kokarin farfadowa ne daga fiye da shekaru 10 da tayi tana fama da matsin tattalin arziki musamman ma bisa ci gaban da aka samu a wannan bangaren na hakar ma'adinai. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China