in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da wasu sababbin ministoci a Masar
2013-07-23 14:38:30 cri
An ci gaba da tsara ayyukan hukuma da mahukuntan gwamnatin rikon kwaryar kasar Masar ke yi, a ranar Litinin 22 ga wata wasu sabbin ministoci uku sun yi rantsuwar kama aiki, wadannan ministocin sun hada da na ma'aikatar shari'a Adel Abdel-Hamid, da na sufuri Ibrahim al- Dimery, da kuma na ma'aikatar habaka ayyukan hukuma Hany Mahmoud.

A kuma ranar Lahadin data gabata ne majalissar ta zartaswa ta yi zamanta na farko ba tare da wakilcin ko da mutum guda daga jam'iyyar 'yan uwa musulmi ba.

A ranar Asabar din da ta gabata, yayin da yake amsa tambayoyi cikin wani shiri da gidan talabijin din kasar ya yada, firaministan rikon kwaryar kasar ta Masar Hazem al-Beblawi, ya yi kira da a kawo karshen rarrabuwar kan dake addabar kasar a halin yanzu, yana mai cewa lokaci yayi da za a gudanar da sulhu, a kuma dinke barakar dake tsakanin al'ummar kasar. Bugu da kari Al-Beblawi ya jaddada cewa aikin gwamnatin ta wucin gadi bai wuce kafa kyakkyawan ginshiki ga zababbiyar gwamnati mai zuwa ba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China