in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar hukumar gudanarwa ta kungiyar AU ta gana da jakadan musamman na kasar Masar
2013-07-23 10:46:09 cri
A ranar litinin shugabar hukumar gudanarwa ta kungiyar hadin kan kasashen Afirka AU Nkosazana Dlamini Zuma ta gana da jakadan musamman na gwamnatin wucin gadi a kasar Masar Mona Omar a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.

Jakadan na Masar ya gabatar da matsayin gwamnatin kasar dangane da mataki da kwamitin tsaro da zaman lafiya na kungiyar AU ya tsayar a ranar 5 ga watan Yuli 2013, wanda ya dakatar da kasar Masar daga kungiyar AU har sai ta dawo kan tsarin dokokin kasa.

Omar har wa yau ya nemi karin haske kan kwamitin bincike da kungiyar AU ta kafa daga bisani kan kasar Masar da kuma ayyukan da zai gabatar.

Kwamitin binciken na musamman da shugabar gudanar da kungiyar AU ta kafa dangane da hali da ake ciki a kasar Masar, ya yi zaman shawarwari na farko ran 16 ga watan Yuli a Addis Ababa.

Yayin jawabi ga 'yan jarida bayan ganawar tasu, jami'an biyu sun bayyana cewa sun yi tattaunawa kuma sun cimma matsaya.

Zuma ta ce kwamitin zai kai ziyara kasar Masar don ganawa da masu ruwa da tsaki kana zai dawo da rahoto ga kwamitin tsaro da zaman lafiya na kungiyar.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China