in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban rukon kwaryar Masar ya kafa kwamitin gyaran fuska ga kudin mulkin kasar
2013-07-21 15:44:11 cri
Rahotanni daga Masar na bayyana cewa shugaban wucin gadin kasar Adli Mansour, ya kafa wani kwamitin alkalai da kwararru ta fuskar shari'a, domin aikin gyaran fuska ga kundin mulkin kasar, matakin da ake sa ran zai bada damar sake maida kasar kan turbar dimokaradiyya.

Cikin wadanda aka nada domin gudanar da wannan muhummin aiki hadda mai baiwa shugaban kasar shawara kan kundin mulkin Ali Awad Saleh, wanda aka nada matsayin babban jami'in tsare-tsaren aikin kwamitin. Ana sa ran cewa wannan kwamiti zai fara gudanar da ayyukansa a ranar Lahadin nan, a helkwatar rusasshiyar majalissar kolin kasar.

Wannan dai mataki daya ne daga matakan da sojojin kasar suka bayyana dauka, da amincewar ragowar jam'iyyun siyasar kasar da malaman addinai, don gane da warware matsalolin kasar, biyowa bayan tsige tsohon shugaban kasar Mohammed Morsi daga mukaminsa a farkon wannan wata na Yuli. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China