in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Masar ta sanar da yin bincike kan Mohamed Morsi
2013-07-14 17:14:16 cri
A ranar 13 ga wata, kasar Masar ta sanar da fara bincike kan laifuffukan da ake zargin tsohon shugaban kasar Mohamed Morsi da aikatawa. Bangaren masu binciken sun bayyana cewa, ana zargi Morsi da aikata laifuffukan yin ayyukan leken asiri, tada zaune tsaye, kawo illa ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar da dai sauransu.

Bisa labarin da gidan telebijin na Al Jazeera ya bayar, an ce, ofishin masu gabatar da kararraki na kasar Masar ya bayar da wata sanarwa a ranar 13 ga wata, inda ya bayyana cewa, ya samu wasikar zargin Morsi, da ragowar jigajigan 'yan rajin kishin Islama 8 ciki hadda jagoran kungiyar 'yan uwa musulmi Mohamed Badie. Bisa sakamakon binciken da ake yi, akwai yiwuwar tsai da kudurin gabatar da wadannan mutane a gaban kotu.

Bisa al'ada dai, bangaren masu gabatar da kararraki ya sanar da kudurin gabatar da wadanda ake zargi gaban kotu a fili.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, bangaren masu gabatar da kararraki bai bayyana sunan wanda ya gabatar da sakon korafin ba. kamfanin dillancin labaru na Reuters ya bayar da wani labari dake nune cewa, bisa dokokin kasar ta Masar, bangaren masu gabatar da kararraki na iya fara yin bincike bisa takardar zargi da 'yan sanda ko fararen hula suka gabatar.

A kwanakin baya, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Amurka Jen Psaki ta bayyana bukatar hukumomin a kasar Masar da su saki tsohon shugaban kasar Morsi tare da dakatar da kama shugabannin kungiyar 'yan uwa musulmi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China