in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu goyon bayan tsohon shugaban kasar Masar Morsy sun sake yin zanga-zanga a birnin Alkahira
2013-07-20 16:38:33 cri
A ranar 19 ga wata a Alkahira, babban birnin kasar Masar, masu goyon bayan tsohon shugaban kasar Mohamed Morsy fiye da dubu 10 sun yi zanga-zanga don nuna adawa ga bangaren soja da ya soke shugaba Morsy daga mukaminsa, kuma suka bukaci da a mayar da Morsy kan mukamin nasa.

A wannan rana, masu goyon bayan Morsy sun yi taru a birnin Alkahira don yin zanga-zanga, inda sakamakon haka, an samu matsalar zirga-zirgar motoci a wasu yankunan dake birnin. An jibge sojojin kasar a muhimman wuraren da suka yi zanga-zanga, kana an kange wasu hanyoyin motoci.

A wannan rana da yamma a wajen masallacin Azhar, masu goyon bayan Morsy da masu adawa da shi sun yi arangama, amma babu wanda ya ji rauni. A maraicen ranar, masu goyon bayan Morsy sun yi rikici tare da bangaren soja na kasar a dab da fadar shugaban kasar, kuma 'yan sanda sun harba barkonon tsohuwa ga masu zanga-zanga.

Ban da birnin Alkahira, masu goyon bayan Morsy sun yi zanga-zanga a birnin Alexandria, Mansoura da sauran biranen kasar, an kuma samu rikice-rikice a wasu wurare. Bisa labarin da aka bayar, an ce, mutane a kalla 2 sun mutu kana mutane 7 sun ji rauni a sakamakon rikicin da aka samu a birnin Mansoura na kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China