in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan rikon kwaryar kasar Masar ya yi kira da a dinke barakar dake tsakanin al'ummar kasar
2013-07-21 16:04:36 cri
A ranar 20 ga wata, Firaministan rikon kwaryar kasar Masar Hazem Al-Beblawi ya yi kira da a dauki matakan aiwatar da sulhu tsakanin sassan al'ummar kasar, yana mai bayyana muhimmancin hakan, musamman a wannan lokaci da ake ta arangama tsakanin masu ra'ayin kawo sauyi, da magoya bayan hambararren shugaban kasar Mohammed Morsi.

Al-Beblawi ya yi wannan tsokaci ne yayin tattaunawarsa ta farko da gida talabijin mallakar gwamnatin kasar. A cewarsa yanzu haka kasar Masar na tsaka da wani irin yaki na farfado da tattalin arzikinta, da kuma maido da kyakkyawan yanayin tsaro. Bugu da kari Beblawi ya ce, an gudanar da dukkanin nade-naden mukaman da aka yi cikin sabuwar gwamnatin kasar ta rikon kwarya ne bisa cancanta da kuma lura da kwarewar jami'an.

Wannan dai kalamai na Firaministan rikon kwaryar na zuwa ne daidai lokacin da magoya bayan hambararren shugaban kasar Morsi, ke ci gaba da zaman dirshan, tare da gudanar da zanga-zangar kin amincewa da sauke zababben shugaban, ta hanyar abin da suka kira haramtaccen juyin mulkin soji.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China