in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta kafa wata cibiyar al'adunta a Afrika ta Kudu
2013-04-02 10:31:22 cri
Tarayyar Najeriya za ta kafa wata cibiyar bunkasa al'adunta da samar da bayanai a kasar Afrika ta Kudu domin karfafa dangantakar al'adu tsakanin kasashen biyu, in ji ministan yawon bude ido, al'adu da makomar kasa na Najeriya mista Edem Duke.

A cewar ministan, za'a kafa wannan cibiya kafin karshen wannan shekara, bayan bude cibiyoyin al'adun kasar a kasashen Brazil da Sin a shekarar 2008 da 2012.

Cibiyar za ta taimakawa wajen karfafa dangantakar al'adu tare da Afrika ta Kudu, har ma tare da sauran kasashen dake kuriyar Afrika, in ji mista Duke, tare da bayyana cewa wannan zabi an yi shi ne ta la'akari da rawar da Najeriya ta taka a cikin tarihin wadannan kasashen Afrika dake wannan shiyya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China