in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin firaministan kasar Sin ya gana da firaministan kasar Habasha
2013-05-25 16:36:31 cri
Mataimakin firaministan kasar Sin Wang Yang ya gana da firaministan kasar Habasha Haile Mariam Desalegne wanda ke rike da shugabancin karba-karba na AU a birnin Addis Ababa fadar gwamnatin kasar Habasha kuma cibiyar kungiyar AU, a lokacin da ya halarci taron musamman na bikin cika shekaru 50 da kafuwar kungiyar hada kan kasashen nahiyar Afrika.

Da farko dai, Wang Yang yi isar da gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping da firaministan kasar Li Keqiang zuwa ga Haile Mariam Desalegne, sannan ya ce, ya kamata, Sin da Afrika sun hara hadin gwiwa tsakaninsu a dukkan fannoni.

A nasa bangaren kuwa Haile Mariam Desalegne ya yi maraba da zuwan Wang Yang tare kuma da yabawa taimakon da Sin take bayar wa wajen raya kasar Habasha har ma da kasashen Afrika, yana fatan kara hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban-daban. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China