in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin firaministan kasa Sin ya gana da shugabar kwamitin AU
2013-05-25 16:35:16 cri
Jiya Juma'a 24 ga wata, wakilin musamman na shugaban kasar Sin kuma mataimakin firaministan kasar Mr Wang Yang ya halarci taron koli na musamman bikin cika shekaru 50 da kafuwar kungiyar hada kan kasashen nahiyar Afrika, inda ya gana da shugabar kwamitin AU Madam Nkosazana Dlamini-Zuma a cibiyar AU dake birnin Addis Ababa hedkwatar kasar Habasha.

A lokacin ganawar, Wang Yang ya ce, kafuwar wannan kungiya ya amfana ma kasashen Afrika wajen samun 'yanci, hadin gwiwa, kwanciyar hankali da wadata, sannan ya taka rawa wajen daga matsayin kasashen Afrika a duniya don haka kasar Sin na fatan kasashe da jama'ar Afrika su yi amfani da zarafi mai kyau yanzu domin kara sa kaimi ga ra'ayin Pan-Afrika, da samun bunkasuwa cikin lumana yadda ya kamata.

A nata bangaren Madam Nkosozana Dlamini-Zuma ta bukaci Wang Yang da ya isar da godiya da gaisuwarta zuwa ga Shugaba Xi Jinping, tare kuma da yin maraba da zuwan Wang Yang domin halartar wannan taro na musamman, sannan kuma tana fatan kara hadin kai da kasar Sin a fannoni daban-daban. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China