in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kiyasin cewa, jimlar GDP ta kasar Sin za ta karu da kashi 8 bisa dari a shekarar 2013
2013-04-27 15:23:59 cri
Cibiyar nazarin kimiyyar al'ummar kasar Sin ta fitar da wani rahoton tattalin arzikin kasar na yanayin bazara na shekarar 2013 a ran 26 ga wata a nan birnin Beijing, inda aka kiyasin cewa, jimlar GDP ta kasar Sin za ta karu da kashi 8 bisa dari cikin wannan shekara.

Game da wannan ma'aunin tattalin arzikin kasar a wannan shekara, rahoton ya ce, wasu alkaluma sun samu karuwa ciki hadda yawan kudi da aka zuba, cinikayyar shige da fice, ma'aunin yawan sayayya (CPI) idan kwatanta da na shekarar bara, amma yawan kudin da aka kashe wajen sayen abubuwa ya ragu.

Rahoton ya nuna cewa, komawa bayan tattalin arziki da aka samu daga shekarar 2012 na da dalili da tsarin da aka bi na canja hanyar samu bunkasuwa bisa matakai-matakai.

Mataimakin shugaban sashi mai bincike tattalin arziki na cibiyar Li Xuesong ya nuna cewa, a takaice dai, Sin za ta samu karuwar tattalin arziki, da karuwar farashin kayayyaki yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China