in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana iya sa rai cewa GDP da kudin shiga na kowane mutumin Sin su ninka sau daya a shekarar 2020 bisa na shekarar 2010
2012-12-06 16:30:51 cri
Bisa rahoton da cibiyar binciken kimiyya ta kasar Sin ta bayar a ranar Laraba 5 ga wata, an ce ana iya sa rai cewa za a cimma burin da aka fitar a babban taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 18 na cewa, GDP da kuma yawan kudin shiga da kowane mutumin kasar Sin zai samu a shekarar 2020 za su ninka sau daya bisa na shekarar 2010.

Rahoton ya yi kiyasin cewa, a kokarin cimma wannan buri, dole ne saurin karuwar GDP ya kai kashi 7.1 cikin dari a kowace shekara. A shekaru 10 masu zuwa kuma, saurin karuwar GDP zai kai kashi 7.5 zuwa 8 cikin dari a kowace shekara.

Ban da haka, rahoton ya ce, a shekarar 2012, a kuma lokacin da ake fuskantar matsalar basusukan kasashen Turai da raguwar bunkasuwar tattalin arzikin duniya, Sin ta gamu da matsaloli da yawa wajen bunkasa tattalin arziki. Amma bisa karuwar bukatun cikin gida, yawan jarin da aka zuba ya karu cikin sauri. Dadin dadawa, a sakamakon rashin samun farfadowar tattalin arziki ta kasashe masu sukuni, bukatu daga ketare sun ragu sosai. Duk da haka dai, ana cikin yanayi mai kyau na neman samun guraben aikin yi, yawan kudin shiga na jama'ar kasar Sin na karuwa cikin sauri, yayin da hauhawar farashin kayayyaki ya ragu. Wannan ya yi nuni da cewa, kawo yanzu ana cikin hali mai kyau a fannin tattalin arziki a kasar.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China