in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan GDP da kasar Sin ta samu a farkon watanni 3 na bana ya karu da kashi 7.7 cikin 100 bisa na makamancin lokaci na bara
2013-04-15 16:34:26 cri
Bayan samun koma baya cikin watanni 21 a jere, a karshen watanni uku na shekarar 2012, tattalin arzikin kasar Sin ya fara farfadowa, kuma a farkon watanni uku na shekarar bana, tattalin arzikin kasar Sin ya rasa samun bunkasuwa da sauri.

Kakakin hukumar kididdiga ta kasar Sin Sheng Laiyun ya nuna a yau ranar 15 ga wata a nan birnin Beijing cewa, jimlar GDP ta kasar Sin a cikin farkon watanni uku na shekarar bana ta kai kudin Sin Yuan biliyan 11885.5 wanda ya karu da kashi 7.7 cikin dari bisa na makamancin lokacin bara.

A ganinsa, a cikin watanni uku da suka gabata, Sin ta nace kan manufar samun bunkasuwa mai karko, kuma za ta mai da muhimanci don kara samun inganci da moriya a fannin bunkasa tattalin arziki, da kyautata manufar yin kwaskwarima da sa ido kan manyan sauye-sauye, tare kuma da kawo wasu sabbin gyare gyare kan ayyukan gwamnati, sannan da karkata hanyar samun bunkasuwar tattalin arziki ta yadda za a samu bunkasuwar tattalin arzikin kasa cikin daidaici.

Sheng Laiyun ya ce, abin da ya fi muhimmanci da za a yi nan gaba shi ne samun bunkasuwa mai karko da sa kaimi ga bunkasa tattalin arzikin kasar yadda ya kamata, da kuma kyautata zaman rayuwar jama'a. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China