logo

HAUSA

Shugaban majalisar dokokin Kenya zai ziyarci kasar Sin

2024-09-19 14:42:25 CMG Hausa

Bisa goron gayyatar da shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin Zhao Leji ya mika masa, shugaban majalisar dokokin kasar Kenya Moses Masika Wetangula, zai jagoranci tawagar jami’an kasarsa domin gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin daga ranar 21 zuwa 26 ga watan nan. (Bilkisu Xin)