Xi ya karbi bakuncin babban taron tattaunawa kan ci gaban duniya
2022-06-24 20:24:43 CMG Hausa
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya karbi bakuncin babban taron tattaunawa kan raya kasa da kasa, wanda aka bude Juma'ar nan ta kafar bidiyo, bisa taken "Samar da hadin gwiwar raya duniya a sabon zamani, a kokarin aiwatar da ajandar samun ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030 tare."
Shugabannin kasashen BRICS da shugabannin kasashen da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa da abin ya shafa, da kasashe masu tasowa ne ke halartar taron. (Ibrahim)