in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ba za ta shiga tsakani a takaddamar dake tsakanin Oatar da wasu kasashe hudu ba
2017-08-31 13:11:28 cri
A jiya Laraba ne, ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavlov ya bayyana a birnin Doha, fadar mulkin kasar Qatar cewa, kasar Rasha ba za ta shiga tsakani domin warware takaddamar diflomasiyar dake tsakanin Qatar da kasashe hudu da suka hada da Saudiya, da Masar, da Hadaddiyar daular Larabawa da kuma Bahrain ba.

Mr. Lavlov ya bayyana haka ne, a yayin taron manema labaran na hadin gwiwa tsakaninsa da takwaransa na kasar Qatar Sheikh Sabah Al-Khaled Al-Hamad Al-Sabah.

Ya kuma kara da cewa, ya kamata a warware matsalar bisa tsarin kungiyar hadin gwiwar kasashen yankin Gulf wato GCC.

A nasa bangare, Mr. Al-Sabah ya jaddada cewa, ya kamata a warware matsalar ta hanyar shawarwari tsakanin bangarori daban daban, don tabbatar da tsaron kasar Qatar da kasashen yankin Gulf.

A farkon watan Yuni na bana ne, kasashen hudu suka katse huldar diflomasiya tsakaninsu da kasar Qatar bisa zargin cewa, kasar Qatar tana goyon bayan 'yan ta'adda, lamarin da ke haifar da barazana ga yanayin tsaron yankin, zargin da Qatar din ta musanta, haka kuma, kasashen hudu suka fara hana jigilar kayayyaki a tsakaninsu da kasar Qatar. Daga bisani kuma, wasu kasashe suka sanar da katse huldar jakadanci da kasar ta Qatar.

Amma har yanzu, ba a kai ga sassauta wannan matsala ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China