in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Qatar ta ce ba za ta gurgunta moriyar 'yan kasashen da suka katse huldar jakadanci da ita ba
2017-06-12 10:37:55 cri
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Qatar a jiya Lahadi ta bayyana cewa, kasar ba za ta gurgunta moriyar mutanen da ke kasar, wadanda kasashensu suka katse huldar jakadanci da ita ba.

Sanarwar da ma'aikatar ta fitar a wannan rana ta yi nuni da cewa, Qatar ba za ta dauki matakai kan mutanen da ke cikin kasar, wadanda kasashensu suka katse huldar jakadanci da ita ba, haka kuma ba za ta dauki matakai na rage matsayin huldar jakadanci da su ba.

Sanarwar ta jaddada cewa, 'yan kasashen da suka katse huldar jakadanci da kasar Qatar, wadanda suke rayuwa a cikin kasar suna da cikakken 'yanci.

A labarin da aka bayar, an ce, kasashen Saudiyya, da hadaddiyar daular Labarawa, da ma sauran wasu kasashe tuni sun bukaci al'ummarsu da su bar Qatar, haka kuma sun bukaci mutanen kasar Qatar da su fita daga kasashen cikin kwanaki 14 tun bayan da aka katse huldar jakadancin.

Kwanan nan kasashen Bahrain da Saudiyya, da hadaddiyar daular Larabawa, da Masar, da Yemen, sun sanar da katse huldar jakadancin da kasar Qatar, inda suka zargi Qatar da nuna goyon baya ga ayyukan ta'addanci, tare kuma da lalata zaman lafiya a shiyyar.

A game da wannan, ma'aikatar harkokin waje ta Qatar ta bayyana bakin cikinta, tana mai cewa, wannan mataki ko kadan ba shi da dalili. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China